YADDA ZAKI MALLAKE MIJIN KI!!! SHAWARWARI ASHIRIN (20)


Godiya ta tabbata ga Allah shi kadai babu abokin tarayya, Tsira da Aminci su tabbata akan wanda babu wani Annabi bayansa, da iyalan gidansa da sahabbansa da wadanda suka biyo bayansu da kyautatawa har zuwa rana sakamako. Bayan haka;
Wannan wata nasiha ce  da aka gabatar a wajen walimar wata daga cikin ‘yan uwa (Allah ya bata zaman lafiya).
Kamar yadda yake, mata na kaunar ace sun mallake zukatan mazajen su, ta yanda kowane lokaci mazajen suna jin dadin zamantakewar su da matan kuma suna kaunar su matuka, ta yanda wannan yakan kai wasu matan zuwa ga halaka ta hanyar neman wannan (mallake mazajensu) inda wasu ke zuwa wajen bokaye da malaman tsibbu. To ‘yar uwa albishirin ki, zaki iya mallake mijin ki ta hanyar da addini ya yarda, wannan hanya itace kyautata mu’amala tsakanin ki da shi, kamar yadda wani mai hikima yake cewa acikin wasu baitoci;
Ka kyautatawa mutane zaka mallake zuciyar su, saboda sau da yawa kyautatawa ta kan bautar da mutum (wajen wanda yake kyautata masa).
Ga wadansu wasiyyoyi da shawarwari da idan ‘yar uwa tayi aiki dasu zata mallake zuciyar mijin ta cikin ruwan sanyi, gasu kamar haka;
1. Ki yiwa mijin ki da’a kuma kada ki sabawa umarnin sa, sai dai fa idan ya bukaci ki aikata abinda Allah (SWT) ya haramta, saboda babu da’a ga abokin halitta wajen saba wa mahalicci, idan ya umarce ki da sabon Allah, ki kame kada ki aikata, kuma kiyi amfani da hanyar da tafi dacewa wajen yi masa nasiha da fahimtar dashi har ya canza ra’ayinsa akan wannan.
2. Ki yi mu’amala dashi da hanya mai kyau, da zance mai dadi, sa’annan ki rika sanya yabo da jinjina da addu’a a cikin zancen ki, kamar, Allah ya kara maka lafiya, Allah ya kiyaye min kai, da dai makamantan su.
3. Ki rika yi masa kyaututtuka wani lokaci, komi kan kantar ta, domin kyauta na kara aminci da kauna, kamar yadda Annabi SAW yace: kuyi kyauta, zaku so junan ku.
4. Ki kasance koda yaushe cikin shiga mai kyau (ba sai lokacin da zaki biki ba ko anguwa) kuma ki kula koda yaushe kada ya samu abinda baya kauna daga wajen ki, saboda kulawar mace da tsaftar jikin ta da kwalliyar ta yana daga cikin manyan sabubban da zasu sa so da kauna tsakanin ma’aurata.
5. Ki fahimci dabi’ar mijin ki da yanayin shi (kamar tsanani, saurin fushi, rashin son hayaniya, da makamantan su) saboda ki nisanci ababen da suke sabanin dabi’ar sa, ko kuma wadanda suke janyo fushinsa ko bacin ransa.
6. Ki kula da ababen da yake sha’awa kuma yake so, kuma ki maida hankali wajen kulawa dasu, saboda kowane miji yana da wasu ababe da yake sha’awa kuma yake so, mace mai wayo tana fahimtar cewa yi masa ababen da yake so kuma yake sha’awa itace hanya mafi sauki wajen samun kaunar sa da kuma jin dadin zaman aure da shi.
7. Ki kula sosai wajen sabuntawa da chanji acikin abubuwan ki, kama daga wajen qawata daki, da jeren ki, da girki (musamman), saboda tsayawa akan hanya daya kawai yakan kawo qosawa da gajiyar miji har ya kai baya sha’awar abubuwan da kike yi.
8. Ki guji yawaita qorafi, saboda mafi qyamatuwar mace a wurin maza itace mace mai yawan korafi, abun ma yakan kara muni idan qorafin ya kasance a gaban wasu kike yi, kamar makwabta, da danginsa ko naki.
9. Idan mijinki ya aikata maki abinda bakiji dadin sa ba ko ya bata maki rai, kada ki yi masa fada ko ki daga sautin ki saman nasa a gaban mutane, ko yaransa, ko kuma a wajen da akwai mutane ko ake jin sautin ki. Amma ki bari sai kin kebanta daga ke sai shi, kuma kinga ya sauko (idan fushi yakeyi), kuma kiyi masa Magana da murya mai taushi, da kalamai masu tasiri, a wannan lokacin zai baki dukkan hankalinsa ya saurare ki kuma yay i maki abinda kike so, da yawan mata suna samun matsala da mazajensu saboda sun jahilci wannan hakikar.
10. Idan mijin ki bai yi maki abin da ya kamata yayi maki ba, ko kuma kina da bukatar wani abu daga gareshi, to gabani ki nema ki fara gabatar da wasu kalamai wadanda suka kunshi yabo da jinjina da kuma ambaton halayensa masu kyau, sannan ki ambaci bukatar ki, kashedin ki da inkari (musun) alkhairin da yayi maki, saboda wannan yana daga cikin Butulcewa abokin zama (kamar yadda Annabi SAW ya nuna), kuma wannan yana daga cikin abinda ke bata kauna tsakanin ma’aurata.
11. Ki qawata rayuwar ki ta aure da nuna kauna da soyayya ga mijinki da zantukan ki kuma aikin ki ya nuna hakan, kada ki sanya rayuwar ki busassa ta yadda baki nuna masa so ko kauna, saboda rashin nuna masa so da kauna, da yawaita mashi matsaloli a cikin rayuwar ku ta aure, shine ke sanya yawancin maza fita waje domin neman wanda zai nuna masu kauna, daga karshe ya kawo maki abokiyar zama (wadda zata yi mashi wannan).
12. Kada ki cika neman abubuwa daga mijin ki musamman bukatun da suka shafi KUDI, sannan ki kasance mai lura da yanayin da miji yake ciki (misali bai amshi albashin wata biyu ba, ko ana damun sa da kudin haya ko bashi da sauransu), sannan bukatar ki ta kasance cikin lokacin da ya dace, ba lokacin da yake son ya huta ba ko sadda yake cikin damuwa, sannan bukatar ta zama wadda babu makawa sai any ice, saboda maza bas a son mace mai yawan naci da neman bukatu dare da rana.
13. Ki kula da umarnin mijin ki a halin tafiyar sa da sadda yake gida, sannan kada ki saba masa koda a cikin abubwa masu sauki ne, sannan kada ki yada sirrin sa, kuma kada ki ambaci nakasun sa da aibinsa ga kowa ko meye kusancin ki dasu, sannan ki rika ambaton sa da alkhairi a wajen wasu, (ki tuna da qissar Annabi Ibrahim AS da matan dansa Isma’il AS), yin hakan zai sanya ya kara aminta da ke, sannan tona masa asiri da aibata shi ba abinda zai jawo maki illa rashin ganin girman ki da shi mijin zai yi da kuma wautar da ke da walakanta ki da sauran mata zasuyi.
14. Ki dogara ga Allah sannan kuma ki yarda da kanki wajen walwale matsalolin gidan ki, kashedin ki da fitar da matsalolin ki waje, ko kuma gun kawaye, sannan kiyi amfani da duk hanyoyin da suka dace wajen walwale su, saboda ita matsala idan ta fita ta yadu ta girmama sai shaidan ya shiga ciki, Allahumma sai in matsalar ta fi karfin ki sai ki nemi shawarar ma’abota addini da masu hikama wajen walwale ta.
15. Ki cika rayuwar mijin ki da dukkan komai, kuma ki yi musharaka da shi wajen damuwarsa, da farin cikin sa, kuma ki saba masa da yin dukkanin abubuwan sa hatta yi masa hidima cikin kananan abubuwa, haka zai sa idan ya fuskanci wata matsala zai dawo gareki don neman shawara, kuma zai kasance mai bukatuwa gareki a cikin dukkanin lamuran sa.
16. Kashedin ki da zama WALLAAJAH: wadda take fita da zarar mijin ta ya fita, fitar ki daga gida ta kasance sai in bukata mai girma ce ta taso, kuma idan zaki fita ki nemi izini sa, sawa’un yana gari ko yayi tafiya, saboda yawan fitar mace daga gidan mijin ta yana raunana alaka tsakanin su, kuma wannan shine ke sanya mace ta rika barin aikata abinda ya dace tayi cikin gidan ta.
17. Kada ki kasance mai son abin duniya acikin tasarrufin ki da mu’amalolin ki da mijin ki, sannan idan kika ba mijin ki wasu kudi ko kika yi masa alkhairi, kada ki yi masa gorin abinda kika yi masa, saboda wannan zai cutar dashi, kuma idan Allah ya baki abin da zaki yiwa kanki lalura kada ki takura kice sai yayi maki, kuma ki kasance mai karamci a wajen kyauta.
18. Ki qawata kanki da kunya da muru’ah acikin mu’amalar ki da mijin ki, kuma ki kasance mai kyawawan dabi’u, ki nisanci zagi, ki sanya mijin ki ya ji nauyin ki saboda kirkinki, idan kuma yay i abinda kika kyamata daga gareshi, ki sanya shi ya fahimci haka daga fuskar ki, saboda wannan uslubi yana da tasiri sosai.
19. Ki aikata abubuwan da zasu sa mijin ki ya aminta da ke, kada li yaudare shi, kuma kada ki munana zato gareshi, kada ki saurari waswasin shaidan da maganganun kawayen ki (munanan kawaye), domin duk sadda mace ta bada kunnen ta domin sauraren wannan, to kofar sharri babba ce take budewa kanta, wanda wannan yana iya kiawa ga rabuwa (wal’iyazubillah).
20. Ki kasance mai fadin gaskiya tare da mijin ki a koda yaushe, a kuma cikin komai, kuma ki sanar dashi duk abinda ke faruwa a cikin rayuwar ki, kuma idan wata matsala ta faru ki sanar dashi tun farko ba sai lamari ya ta’azzara ba daga bisani ki sanar da shi, saboda wannan zai iya kawo mummunan zato da kuma zargin ki akan hakan.
Daga karshe ki kula da duk abinda zai qarfafa alaqa tsakanin ki da mijin ki, ki nisanci duk abin da zai raunana ta ko ya gusar da ita. Ina rokon Allah ya albarkaci matan musulmi, a duk inda suke ya kara alakar so da kauna tsakanin su da mazajen su.
Dan uwanku:
Mustafa Yakubu Lugga

Comments

Popular posts from this blog

KYAKKYAWAN KARSHE DA MUMMUNAN KARSHE

KA KOYI LADABIN ILIMI KAMAR YANDA KAKE KOYAN ILIMI.